
..................
TALALA...............
Mai kamar Sake............................
.....Written by : Jazuli Ya'u Hashim......
......“Ai wato Hajiya, ina fad'a miki idan kayan nan
suka samu isowa cikin qasar nan, a daidai
wannan lokacin, za mu samu gwagwa6ar riba
mai yawa, wadda ba mu ta6a samun irinta ba”.
Inji Alhaji Nasiru Damisa, wanda yake zaune a
qayataccen katafaren d'akin hutawar gidansa,
cikin tsananin farin ciki yake sanar da matarsa
Hajiya Saudatu hakan wadda take zaune a kusa
dashi a kan kujera. “ Ai da ma tunda naga
bakinka yaqi rufuwa, na san cewa dawalakin goro
a miya, domin kuwa dalilin farin cikinka, ruwa
baya tsami banza”. Qir… wayar Alhaji Nasir ta
fara yin gunji a cikin aljihunsa, yasa hannu ya fito
da ita waje, Musa Bala sunan da ya bayyana
kenan akan fuskar wayar, alhaji Nasiru ya d'aga
wayar yana murmushi ya kara a kunne “ Hello
Pilot Musa!” “ Alhaji Musa saidai fa ka yi haquri,
domin Jirgin da ya d'auko kayanka, gaba d'aya
ya nutse a cikin teku”. Maganar da Pilot Musa ya
sanar da Alhaji Nasir kenan. Cikin tsananin sauri
alhaji Nasir da Matarsa suka miqe tsaye a fusace
“ Jirgi ya nutse a cikin teku! Innalillahi wa’inna
ilaihirraji’un”. Alhaji Nasir yace hakan lokacin da
gumi ya jiqa masa jiki jirgif, ya cire hular dake
kansa yana fifita da ita, gaba d'aya hankalinsu ya
yi matuqar tashi, a daidai lokacin ne ‘ya’yansa
mata guda biyu masu qananan shekaru, suka
shigo cikin falon daga waje, suna sanye cikin
kayan makarantar Nursery. Yaran suka tsaya
cirko-cirko a falon suka bi iyayensu da kallo cike
da fargaba da kuma mamakin abinda ya faru.
Nan take Alhaji Nasir ya yanke jiki ya fad'i qasa
tim a tsakiyar falon, matarsa da ‘ya’yansa suka
yi kansa a guje suna kuka. “ Abba dan Allah ka
tashi kada ka tafi ka barmu”.Babbar tace haka
cikin muryar kuka tana jijjigashi, Hajiya Saudat da
Surayya suma kukan suke suna jijjiga jikinsa suna
ta iface-iface.
Matashin likitan da shekarunsa ba su wuce
ashirin da biyar a duniya ba, ya bud'e qofar
d'akin jinyar ya shigo ciki daga waje, da sauri ya
qarasa inda marar lafiyar yake kwance akan
gadon,. “ Wannan ai Baba Nasir ne, Docto me
yake damunsa?”. Datta Lawal ya juya ya kalli
Aliyu Haidar matashin likitan da ya masa
tambayar, “ Haidar da ma ka san shi ne?”.
“kwarai kuwa docta, amma me yake damunsa”?.
Haidar ya Tambaya “ ya had'u da mummunan
cutar nan ta mutuwar 6arin jiki”. Inji datta Lawal,
Haidar ya matsa kusa da Marar lafiyan ya qura
masa idanu.
SHEKARU GOMA BAYA.
“ To Alhaji Allah ya kiyaye hanya” Umman mu
Karimatu tace da Abbanmu Alhaji Auwal haka,
lokacin da suke tsaye a jikin motarsa dake
harabar gidanmu, suna yiwa juna bankwana “
Allahumma amin Uwar ‘ya’yana” yace hakan yana
murmushi, sannan ya miqa hannu ta miqo masa
‘yar qaramar jakarsa dake riqe a hannunta, ya
bud'e motarsa ya shiga ya tashe ta, mai gadi ya
bud'e masa get ya fita sannan ya ja get d'in ya
rufe, Umman mu tana inda take tsaye tana bin
motar da kallo har saida ta fita, sannan ta juya
ta koma cikin falo.
Qarfe biyar na Yamma aka kira waya aka sanar
da Umman mu cewa “mijinta wato Abbanmu ya
yi had'ari a hanyar sa ta zuwa garin Abuja kuma
Allah ya kar6i ransa” Haidar dake zaune akan
kujerar bayan tebur yace haka yana bawa datta
Lawal labari, cikin muryar tausayi Haidar ya
cigaba “ A lokacin da Mahaifinmu ya rasu ina aji
uku a wata makarantar sakandire ta kud'i, da
yake Abbanmu ya d'ora rai a kaina, na ganin na
samu kyakykyawan karatu, yayyuna guda biyu
Mata, anti Hassana da anti Nafi kowaccensu
tana gidan mijinta.
Bayan rasuwar mahaifinmu ba dad'ewa, sai
komai ya ta6ar6are mana, talauci ya sako mu a
gaba abincin da za mu ci ma, da qyar muke
samu. A wannan lokacin ne muka bujirowa da
Mahaifiyarmu wata tambaya, game da inda
dukiyar Mahaifinmu take, a lokacin ne Umman ta
mu ta sanar da mu cewa, dukkanin wata dukiya
ta Mahaifinmu, tana Hannun babban Amininsa
Alhaji Nasir Damisa, sun had'a dukiyarsu suna
kasuwanci tare, kafin mahaifinmu ya rasu ya
sanar da ita hakan.
Lokacin da mahaifiyarmu ta je masa da zancen
gadonmu, ya nuna shi sam bai san da wannan
maganar ba, har kotu Ummanmu ta kai qararsa
amma da yake akwai kud'i a hannunsa ba mu
samu nasara ba, haka muka cigaba da rayuwa
cikin quncin talauci, wanda sakamakon hakan ne
yasa dole na bar makarantar kud'i na koma ta
gwamnati, ni da ban san duk wata wahala da
gwagwarmayar rayuwa ba, a wannan lokacin dole
ta sa na shiga fafutukar neman na kaina, na yi
aikin qarfi iri-iri a rayuwata har Allah ya kawo ni
wannan matsayin”. “ Wai da ma Haidar wannan
ne mutumin da ka ce ya cinye muku gadon ku” in
ji datta Lawal “ Qwarai kuwa shi ne”
Haidar ya amsa masa, datta Lawal ya yi shiru
yana yin wani tunani, sannan ya nisa yace “ In
Allah yaso ya yarda lokaci ya yi da dukiyarku za
ta dawo hannunku” Haidar ya zaro ido ya bishi
da kallo cike da mamaki.
Bayan Alhaji Nasir ya dawo cikin hayyacinsa,
Haidar ya bayyana a gabansa tare da tilin
tambayoyi, wanda Alhaji Nasir di'n yaqi amsa
masa, da yake sun shigo da lauya da ‘yan sanda
cikin maganar, hakan tasa dole aka yiwa Alhaji
Nasir wasu allurai da ake kira Narcotic test.
Allurai ne da ake yiwa wanda ake tuhuma da laifi
su idan ya yi taurin kai, nan take Alhaji Nasir ya
fito fili ya fad'i gaskiya, ba su bar wajan ba har
saida Alhaji Nasir ya yi Transfer d'in dukkan
kud'ad'en su haidar na gado a account d'in
Haidar d'in.
Duk lokacin da Alhaji Nasir ya tuna cewa dukkan
dukiyarsa ta nutse a cikin teku, sauran kud'insa
na banki kuma ya turawa Haidar su, sannan ya
had'u da ciwon mutuwar 6arin jiki, sai zuciyarsa
ta buga sosai, a dalilin hakan ne har zuciyarsa ta
fashe ya mutu............................
..............Alhamdulillah..............
0 Comments