Yaro Da Kudi Page 1 Written By Binta Umar

...........YARO DA KUDI.......... WRITTEN BY Binta Umar (MAMAN ABDUL WAHABU).............................. ...Bissimillahi rahamanirrahim.... Nafara da sunan Allah mai rahama mai Jin kai Allahu buwayi gagara Misali. Allah yanda kabani Ikon fara rubun littafin kasa na kammalashi......................... WANNAN LITTAFIN QAGAGENE DAGA NI BINTA BANYI DAN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAIDAI DA YANAYIN RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NE👌🏻.................................. Ban yadda wani ko wata ta juya min littafi ba batare da izini na Dan haka a lura........................................ 💋Bakina bazai iya fadin irin godiyar da take cikin zuciyata ba Amma na barwa zuciyata komai tabbas nasan Akwai so na gaskiya a zuqatanku Ku kun San kan Ku ba sai na fadaba Allah ya bar kauna ta Dan Allah💋.........,.......................... Iyayena Abin Alfaharina Allah yaja min da ranku yakara muku lafiya Ameen👏🏻......... .............Page 1.................... Wani matashin yaro ne zaune cikin Wani haddaden falo dashi da Abokanshi sun kaceme sai har gowa suke gefe guda kuma Abinci ne da Abinsa birjiki gasunan anci an barsu ! "Yana zaune kan kujera cikin wasu kananun kaya da sukayi masa bala'in kyau kafarshi daya kan daya kamar wani mace Hannusa riqe da *Sigari* yana busawa da kangashi Kaga Dan duniya domin ida nunshi a Bude suke dudu shekarunsa baza su haura 24 ba! Yanada kudi sosai domin kafatanin danginshi basusan wani Abu ba waishi talauci "yan boko ne taimi dukkanisu duk Wanda ya kwana yatashi A family nasu sai yayi kararun boko basu damu da yin kara tun Addini ba sosai qalilan daga cikinsu ne suke mai da hankali suyi!! To Shima *NASIR AL'HUSEN* yana cikin jerin waddanda basu damu da karatun Addini ba yafi mai da hankali a boko domin tun yana shekara Sha shida yake can America cikin turawa karatun boko ya samu shekara takwas a can Dan haka duk wasu munanan dabi'u a can ya dauko Abinshi. Idonshi idon Mata ne mutukar ya kyalla ido yaga mace mai kyau nan da nan zai rude zai iya kashe ko nawa ne a kanta domin samun biyan bukatarsa Yana ta6a shaye shaye Amma baita shangiya ba har yanzu suma kayan mayen sai sun fita yawace yawacensu da Abokai yakesha ko in zai nemi matanshi baya ta6a yadda yasha wacce zata bugar dashi dayawa masu tsada yake Amfani dasu Yana 6oyewa iyayenshi duk a zatonsa basu gane ba tuntuni dadyn dinshi ya fahimce shi shi dai kwai yana masa Addu'a Mom d'inshi kuwa Sam bata Fuskanci komai ba dake macece mai son yara kwata kwata batason laifinsa duk Abinda yayi dai dai ne! Shiyasa suke dasawa dashi. Dan yana sakewa da ita sosai bakamar dady nashi ba!!..................................... . MRS AHAMAD GWADABE CE...............

Post a Comment

0 Comments